DASUNAN ALLAH MAIRAHAMA MAIJIN KAI
 HADISAN DA ‘YAN TAWAYE SUKE KARYATAWA KAI 
 TSAYE.
 Kamar yadda akayimin tambaya kuma aka nemi bayani daga wurina , kuma 
hadissan da suka karyata suna da yawa ainun , kuma agaskiya hukuncin duk
 wanda yakaryata Annbi (saw) kafirine kaitsaye, mai karyata Annabi (saw)
 ba’a binsa sallah kuma ba’a cin yankansa, sai in ya tuba yagyara 
,saboda haka ga kadan daga hadisan da suka karyata. 
 ADDU’O’I
 
Acikin sunnanittirmizi hadisi na dubu uku da dari uku da tamanin 3380 
manzon Allah (saw) yace wadansu mutane basu zauna amajalisin da basu 
ambaci Allah cikin saba kuma basuyi salati ga Annabinsuba face wannan 
majalisin yazama hasara garesu ranar qiyama , in Allah yaso ya  
azabtardasu  in Allah yaso saiya yafe musu , tirmizin ya  inganta 
hadisin , haka kuma Albanima ya ingantashi.Saboda haka sai muyita Addu’a
 aduk inda  aka taru da salati wa ma’aiki (saw)
  Saboda haka yazo 
acikin fatahulbari hadisi na 5923 Annabi tsira da amincin Allah 
sutabbata agareshi yace: wadansu  mutane bazasu haduba (wato kowanne 
irin haduwa na musulunci) sashinsu yana Addu’a sahinsu yana cewa Amin 
face Allah  ya karba musu , haka dabarani hadisi na 206 . haka 
faddulwa’aa’I hadisi na 23. haka kuma hadisin Abubakar siddiq alokacin 
daya aiki sa’idu bn Amir ya umarceshi yaje harsaiya samu zaid bn Abu 
safiyan, sai Abubakar yace bayin Allah Kuroki Allah ya tsare  sahibinku 
 da ‘yan uwanku dake  tare dashi , yakubutar dasu, sai ku daga 
hannayenku gaba daya Allah yayi muku rahama , saisuka daga hannayensu 
gaba dayansu su fiye da mutum hamsin 50 sai Aliyu bn Abi dhalib yace : 
damasu musulmi masu yawa bazasu daga hannayensu suna rokon Allah wani 
Abuba face yakarba musu ,matukar basabon Allah suke nufiba  ko yanke 
zumunta . faddul wa’aai hadisi na 13  Haka kuma Ankarbo daga salman yace
 : manzon Allah (saw) yace  wasu jama’a mutane bazasu daga hannayensuba 
zuwa ga Allah Azzawajallasuna rokonsa wani abuba face yakasance hakki ga
 Allah yasanya abinda suka nema acikin hannayensu” hadisi sahihi. Faddul
 wa’aa’I shafina 54
 Wadannan  hadisai dawasunsu sunyi nuni akan addu’ar jam’I duk inda musulmi suka hadu.
 kuma bisa ga maimaita addu’a wa mutanen kirki bizaharil gaibi , kadubi 
suratul hasher ayata 10 inda Allah kecewa (kuma wadanda sukazo abayansu 
suna cewa uban gijinmu kagafartamana kuma da ‘yan’uwanmu wadanda suka 
rigamu imani kuma karka sanya wata gilli acikin zukatanmu gameda wadanda
 suka rigamu imani ) kuma da makamantan wannan ayar kuma asura tul  
Muhammad Ayata  19  da kuma  Ibrahim Ayata 41. Duka  sun bada ma’ana 
guda gameda addu’ar .saboda haka , 
  sai manzon Allah (saw) 
yafassara ayar da cewa “ babu wani bawa musulmi da zaiyi addu’a ga 
dan’uwanshi alhali dan uwannashi  bayanan face mala’ika yace kaima 
anbaka duk irin abinda karokamasa” sahihu muslim hadisi na 7103. Wato 
mana’a “bizaharil gaibi” yazamo wanda akewa addu’ar bayanan awajenda ake
 addu’ar ko yanada rai ko bayi da rai.
  Kuma kadubi hadisin ka’ab bn
 malik wanda maruzi yaruwaito daga ka’ab bn malik yaddar Allah yatabbata
 agareshi , dansa Abdurrahman yana  cewa nine jagoran babana lokacin da 
yamakance , kuma duk lokacinda nafita dashi zuwa juma’a idan yaji kiran 
sallah yana  Addu’a da neman gafara wa sa’ad bn zurrara sai yazamana 
kullum yaji kiran sallar juma’a saiyayi Addu’a wa sa’ad bn zurrara , sai
 yaron yace ya babana meyasa kaketa maimaita addu’a  wa sa’ad bn zurrara
 ko wace juma’a? sai yace ya dana ai shi sa’ad  bn zurrara shine farkon 
limaminda yafara yimana sallar juma’a  Amadina a’unguwar baniibayada, 
kafin Annabi (saw) ya iso daga makkah , sai yaron yace alokacin 
kunawane? Sai ka’ab bn malik yace alokacinmu hansin 50 ne. wannan aiki 
na ka’ab bn malik yana tabbatarda cewa zamuyita maimaita addu’a kenan ga
 magabata mutanen kirki.
  Kuma hadisan ingantattune, sabida haka 
aiki dasu shine bin sunnar ma’aiki (saw) domin sahabi komai yayi ya 
koyane daga Annabi (saw)saboda haka ba’a tuhumarsu da saba mashi. 
 SHAFA HANNAYE AFUSKA
 Tirmizi hadisina 3386) An tabbatar dashi kamar haka acikin “ faddul wa’a’I 54”
 An karbo daga salim dan Abdullahi bin umar daga Abdullahi bin umar daga
 umar dan khaddabi , yaddar Allah ta tabbata agaresu , yace : manzon 
Allah (saw) yakasance idan yadaga hannayensa cikin Addu’a baya saukesu 
saiya shafi fuskarsa dasu . hadisin sahihine . faddul wa’a’I .shafi na 
54
  to aikaga bazamu barsuba muje muna aiki da kame kame marar 
daliliba dan son zuciya ,muje muna cewa malam wane yace wane yace, 
Alhali kuwa  ga ingan tattun hadisai dayawa daga manzon Allah (saw) akan
 wannan mas’ala saboda haka mumanzon Allah (saw) da sahabbansa (Ra) 
mukebi akowace mas’ala. Kuma Allah ya taimakemu akan haka Amin .
 
kuma duk wanda ya karyata hadisan Annabi (saw)  ingantattu irin wadannan
 da gangan harma da ayar Al’qur’ani karara bisa ga maimaita addu’a ga 
bayin Allah  agaskiya yakafurta . kuma ina kira ga ‘yan uwa Ahlussunna 
sulura akwai wadanda suke tahowa da sunan musulunci Alhali kuwa ba 
musulmi bane suna zuwane don subata  akidar musulmai, domin Annabi (saw)
 yace addu’a bargon ibadane, “wato kashin bayan addinine” kenan 
saikalura damaikokarin hanaka addu’a yaya ‘aqidarsa take?.
 NADIN RAWANI
 Nada rawani sunnane kamar yadda aka tambayi Abdullahi bin umar yafada. 
Umdatulqari sharhu sahihul bukhari hadisi na 5805 Ababin rawani mailamba
 na 15 .sunanuttirmizi hadisi na 1736 kuma asaki jela tabaya tsakanin 
kafadu kota gaba kamar yadda Annabi (saw) yake sakewa, kuma sahabbansa 
sukayi koyidahaka . akara duba  .Fatahul bari 16/356
 Sunanun nisa’I  hadisi na 5343zuwa 5344 da 5345 da 5346
 Sunani abi dauda hadisi na 4076 zuwana 4077kuma ga hadisin Rukana 
mainuna inda ma’aiki (saw) yake cewa banbanci  tsakaninmu da mushirkai 
Rawani akan hula .sunani Abi dauda hadisi na 4078
 Sunani ibni majah ,
 hadisi na 3584 zuwa 3585 zuwa 3586 zuwa 3587 kuma cewa rawani al’adar 
larabane kawai ,!!wannan magana jahilcine don bahaka maruwaita hadissan 
suka fahimtaba ,a’a sukam sunfahimci rawani sunnane na ma’aiki (saw) 
kuma gashi mafiyan maruwaitan ba larabawa bane,haka dukkam malamai suka 
fahimci rawani sunnane na ma’aiki (saw) tabbatacce. 
 Wato dai abinda
 yakamata afahimta anan shine Rawanidai sunnane me karfi na Annabi 
Muhammad (saw) kamar yadda ya gudana acikin sahabbai da tabi’iyna da 
tabi’uttabi’iyna har zuwa kan sheikh usman dan fodiyo, idan kadubi 
ihya’ussunnah shafina 148. Shima danfodiyo fahimtarshi rawani sunnane 
mai karfi, wato yabi sahun ‘yan’uwansa malaman sunnah. Saboda haka duk 
mai zagin Rawani to yasani da kyau yana zagin Annabine da sahabbansa da 
tabi’iyna da tabi’uttabi’iyna, kuma ya bautawa son zuciyarsa , da hakan*
 JIYARWA A CIKIN SALLAH
    Hakiqa Bukhari yayi tarjama akan jiyarwa a cikin sallah da fadinsa 
“Babin wanda yajiyar da mutanekabbarorin liman Har yakai zuwa ga 
fadinsa,Abubakar ya kasance yana jiyar da mutane kabbara.Kuma wannan 
shine jamhurin maluma suka kafa hujja dashi akan jiyarwa acikin 
sallah(Fathul Bary 2\259).Daga jabir Allah ya yarda dashi yace “Manzon 
Allah(saw) yayi mana sallah,Abubakar yana bayansa,Idan Manzon 
Allah(saw)yayi kabbara sai Abubakar yayi kabbara domin ya jiyar 
damu”(Muslim Bisharhin Nawawi 2\345) .Imamu Nawawi yace wannan dalili ne
 akan daga sauti don a jiyar da mutane,kuma ya halatta ga mai koyi da 
liman ya bi wannan sauti na mai jiyarwa.Kuma wannan itace Mazhabarmu , 
kuma Mazhabar Jamhur.(Muslim Bisharhin Nawawi 2\355—356 ko Umdatul Qary 
3\216 ko Tirmizi 1\378 koNailal Audar 2\269).
 Ash-shaukani yace ya 
halatta ga mai koyi da liman bin sautin mai jiyarwa.Don haka sunnah ce 
ga mai bin liman ya jiyar da masu sallah kabbarar liman,domin 
Annabi(saw) ya sunnanta haka a Masallacin sa mai Alfarma.Kuma Sahabbai 
da Tabi`ai sunyi ta aiki da wannan sunnah har zuwa wannan lokaci 
namu,kuma a yanzu haka ana aikata sunnar jiyarwa a Masallacin Manzon 
Allah(saw) da yake Madinah mai Alfarma.kuma anyi ijima,I akan haka .to 
kaga duk malaman hadisi fahimtarsu kenan gameda wadannan hadissan,to 
kaga ta yaya za’abar sunnah adawo ana shauraron masu Magana da ka?!!
 
 SADALU
 Acikin musannaf na ibni Abi shaiba wanda ake kira “Al’ahadisu wal’asar”
 jizi’I na daya shafi na 342\343, Anruwaito sadalu daga Hasanul basari 
da ibrahimunnakha’I . Ashafina 395 anruwaito sadalu daga Abdullahi bn 
zubair sahabin Annabi (saw) da tabi’innan . ibni sirina  da sa’eed bn 
musayyib da Abdullahi bn yazid  da sa’eed bn jubair.dawasunsu,kuma 
dukkansu tabi’aine . kuma ga hadisin mu’azu bn jabal wanda Dabarani ya 
ruwaito acin mu’ajjamul kabir juzu’I na 2 shafi na 271 yana cewa : “ 
Annabi (saw) idan yakabbara sallah sake hannunsa yakeyi, awani lokaci 
kuma yakanyi qabalu.sa’annan gakuma aikin mutanen madina gabadaya,wanda 
suka gada daga sahabbai da tabi’iina  da tabi’uttabi’iina , kuma wannan 
hujjane ga dukkan al’umma bisa ijima’in musulmi baki daya  , kamar yadda
 ibni taimiyyah ya bayyana acikin majamu’ul fatawi juzu’I na 20 shafi na
 294 ba’ataba samun wadanda suka karyataba, sai ‘yan tawayenmu ayanzu 
Allah ya shiryesu.
 HADISIN SALLAMA DAYA
 An samu daga Aishatu 
Matar Annabi (saw) tace “Annabi (saw) yana yin sallama guda daya ne 
acikin sallah” Sa`ad ibn Hisham Ibn Amir ya tafi  zuwa ga Abdullahi Ibn 
abbas, ya bashi labari da wannan Magana ta Aishatu cewa Annabi (saw) ya 
kasance yana yin sallama guda ne acikin sallah.Sai Ibn Abbas yace tayi 
gaskiya(Muslim 2\170). A cikin ruwayar Tirmizi “Lallai Manzon Allah 
(saw) ya kasance yana yin sallama acikin sallah, guda daya tagabansa, 
sannan ya karkata kansa  zuwa dama kadan”(Tirmizi 1\320). Daga salmata 
Ibn Ak,wa,i yace “ naga Manzon Allah (saw) yayi sallama guda daya”( Ibn 
Majah 1\297). Don haka, an samu ruwayoyi daga Annabi (saw) cewa yayi 
sallama daya acikin sallah gurare da dama, haka kuma an ruwaito daga 
khalifofi guda hudu, Abubakar da Umar da Usman da Aliyu da kuma sauran 
sahabbai kamar ibn Umar da Anas da ibn aby aufa, da Aishatu matar Annabi
 (saw)da Sa,ad ibn aby Waqqas da salmata bn akawa.u, da jama,a da yawa 
daga Tabi,ai bayan sahabban. Saboda haka ya tabbata kenan Manzon Allah 
yana fita daga Sallah da Sallama daya tak. Sigarta shine ASSALAMU 
ALAIKUM.(Fathul Bary Li ibn Rajab 6\59 ko Aujazul Masalik 2\145 ko 
Umdatul Qary 6\123—124) 
  Imamu Nawawi da Ibn Munzir sunce malamai 
sunhadu kancewa  ba abinda ke wajaba ga mai sallah sai sallama daya tak(
 Muslim Bisharhin Nawawi 3\80 ko Sahihu Fiqhus Sunnah 1\127—326).*
 
Aby Wa`il da Yahya Ibn Wasib da Umar Ibn AbdulAzeez da Hassan da Ibn 
Sirin da Qasim Ibn Muhammad da Aishatu (RA) da Anas da Aby Aliya da Aby 
Raja`ida Ibn Aby Awfi da Ibn Umar da Sa`eed bn Jubair da Suwaidu da 
qaisu ibn Aby hazim, kuma dukkansu an ruwaito daga garesu da Isnadi mai 
kyau, kuma AbdurRazaq ya ambaci Sallama daya daga Zuhuri. Tirmizi yace “
 Jama`a da yawa daga cikin Sahabban Annabi (saw) da tabi’ ai da wasunsu ,
 sun zabi yin Sallama  daya a sallar Farilla”(Nailal Audar 2\343 ).  
Imamu Ahmad ya ruwaito daga Abdullahi Ibn Aby Awfi cewa Annabi (saw) ya 
kasance yana fita a sallah ne da sallama daya tak(Musnad na Ahmad 1\236 
ko irwa il galil *2\32—33).  A cikin wata ruwaya Annabi (saw) ya kasance
 yana fita a sallah da Sallama Daya wajen Fuskarsa akan sharadin 
Muslim.Haka kuma Ibn Majah  da Ahmad da Nisa`i da Tirmizi da Hakeem da 
Ibn Hibban da Darul-Quduni  sun ruwaito da lafazin cewa “Manzon 
Allah(saw) ya kasance yana yin sallama daya ne wajen fuskarsa(Nailal 
Audar 2\341—342).Ahmad yace Salih yace Ibn Muhd yace lalle shi zuhair 
amintacce ne mai gaskiya.Haka kuma Abu Hatim da wasunsu duk sun tabbatar
 da haka, kuma hakika Bukhari ya ruwaito Wannan yana nuna 
amincinsa..Amma Bukhari ya takaita akan fadinsa yayi sallama ba tare da 
ambaton adadi ba, ya dai ce ATTASLIMU ba TASLIMATANI ba,don haka 
ATTASLIMU shine asalin kalmar wato MASDARI.MASDARI kuwa baya Magana akan
 adadi,wato kadan ko mai yawa,don haka sallama daya ta shiga. 
 An 
tambayi Malik akan sallama daya a cikin sallah,sai yace haka al`amarin 
yake.Shugabanni magabata sun kasance suna yin sallama daya ne,sallama 
biyu ta karfafu ne a lokacin Banu Hashim.Laisu yace mun riski shugabanni
 magabata da sauran mutane  suna sallama daya ne a cikin sallah 
“ASSALAMU ALAIKUM”(Mukhtasar Iktilaful Ulama,u Lid Dahawi 1\590kuma 
Ahmad ya ruwaito cewa mutanen Madinah sun kasance suna sallama dayane a 
cikin sallah,kuma yace sallama biyu ta daukaku ne a cikin zamanin Bany 
Hashim ma`ana a cikin Mulkin Bany Abbas.Faruwar sallama biyu daga Kuhfa 
ne wato Iraqi.A wannan lokacin Mutanen Madinah sun kasance suna sallama 
daya ne tak kamar yadda suka gada daga Annabi,sai akai amfani dakarfin 
mulki wajen tilastasu ga sallama biyu .Laisu yace “masu Magana akan 
sallama biyunma, mafiya yawansu sun amince akan idan Mutum ya takaita 
akan sallama daya ta isar masa, kuma sallarsa ta inganta”.saboda haka 
Ibnul-Munzir ya ambaci ijima,I kan sallama daya. An ruwaito daga Ibn 
Umar yin sallama daya ga liman da wanda yake sallah shi kadai, da kuma 
yin sallama uku ga wanda yake Mamu kuma akwai wani tare da shi agefen 
hagu.Malik da Dara-Qudani sun tafi akan haka cikin abinda suka ruwaito 
cewa “Annabi(saw) ya umarcemu da muyi wa limamanmu  sallama, kuma sashin
 mu yayiwa sashi sallama”(Dara Kuduni Hadisi na 1373).Hakika 
Annabi(saw)yayi sallama daya da Abubakar da Umar da Usman da Umar Ibn 
Abdul-Azeez. (mudawwana juzu,I nadaya shafi 196) kuma hadisin 
ingantaccene daga Aishatu(R.A).Hakeem yace hadisin ingantaccene akan 
sharadin Bukhari da Muslim.Hakama Sheikh Ahmad Shakir alokacinda yake 
tahaqiqi kan sunanuttirmizi, yace: sallama daya ingan taccene daga 
Annabi (saw) 
 nikuma inacewa wannan hadisin har ma Albani wanda yake
 ingantawa ko ya raunana yadda yaga dama,  shima ya inganta wannan 
hadisin a cikin sahihu ibnu majah (750). Kuma hakika an ruwaito sallama 
biyu daga Abdullahi Ibn Mas`ud,kenan kaga ashe sallama biyumma akwai 
hadisi * tokaga Ashe sallama daya ko biyu duk wanda kayi sallarka ta 
inganta , saidai sallama daya tafi yawan hadissai ingantattu, shiyasa 
bukari bai ruwaici hadisin sallama biyuba .
 ALQUNUTU
 A alqunutu 
zamu gabatarda hadisin Anas inda yake cewa manzon Allah (saw) yakasance 
yana Alqunutu asallar Asuba harsaida yabar duniya baibariba . Ahmad ya 
ruwaitoshi juzu’ina 3 shafi na 162da ibni Abi shaiba juzi’ina 2 shafi na
 312 musannaf na Abdurrazaq juzu’ina 3 shafi na 110 sharhul Asar na 
dahawi juzu’ina 1 shafi na 244  Assunnan darul quduni juzu’I na 2 shafi 
na Albaihaqi juzi’I na 2 shafi na 201 sharhissunnah na bagawi juzu’I 39 
na 3 shafi 123\124 Al’I’itibar na hazimi shafina 188 zadal mi’ad na 
ibnul  qayyim juzu’ina 1 shafi na 275 nasaburraya juzu’I na 2 shafina 
132 Addinul kalis na imamussubuki juzu’I nz 4 shafi 29 majma’uzzawa’id 
juzu’I na 2 shafi na 162 Al majamu’u na imamunnawawi juzu’I na 3 shafi 
na 504  sahihul bukhari juzu’I na 2 shafi  na 14 fathul  bari juzu’I na 2
 shafi na 621 sunanuttirmizi juzu’I na 1 shafi na  311 tuh
 
 
 
          
      
 
  
 
 
 
 
 
 
 
 
 
 
 
No comments:
Post a Comment